Maras Hoto
Search

Taron Kolin Kasashen Afirka yayi Kiran Da A Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Zimbabwe

02/07/2008

Shugaba Robert Mugabe A Wurin Taron Kolin Kasashen AfirkaKungiyar Tarayyar Kasashen Afirka ta amince da wani kuduri wanda yayi kiran da a kafa gwamnatin hadin kan kasa a Zimbabwe, a bayan zaben da aka yi ta tofin Allah tsine kansa na shugaba Robert Mugabe. Haka kuma shugabannin kungiyar dake ganawa cikin sirri a Masar, sun bukaci da a ci gaba da shiga tsakanin gwamnatin Zimbabwe da 'yan hamayyar kasar.

Talata aka amince da wannan matakin a bayan da kasar Botswana ta gabatar ad wata sanarwa mai zafin lafazi wadda ta nemi da a kori Zimbabwe daga tarurrukan Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka da na Kungiyar Raya Kasashen Kudancin Afirka. Mataimakin shugaban Botswana, Mompati Merafhe, ya ce zaben fitar da gwani na makon jiya a kasar Zimbabwe bai tabbatar da halalcin gwamnatin shugaba Robert Mugabe ba.

Jami'an diflomasiyya a taron da aka yi cikin sirri, sun ce su ma shugabannin kasashen Nijeriya da Liberiya da Saliyo sun yi magana da lafazi mai karfi kan rashin halalcin zaben na Zimbabwe.

Wani kakakin gwamnatin Masar, Hossam Zaki, ya ce shugaba Mugabe yayi jawabi mai tsawo lokacin taron, inda ya fito da kakkausar harshe sukar kasashen Afirka da suka soki lamirinsa.

Tun fari talatar nan, shugabannin jam'iyyar hamayya ta MDC da na jam'iyyar ANU-PF mai mulkin kasar sun nuna cewa ba su da sha'awar ci gaba da tattaunawar siyasa. A cikin wata sanarwar da aka bayar a Harare babban birnin kasar, sakatare janar na jam'iyyar MDC, Tendai Biti, ya ce zaben bogi da aka ce an gudanar ranar 27 ga watan Yuni ya kawar da duk wata damar zaunawa don warware rikicin siyasar Zimbabwe.

Shi ma da yake magana a wurin taron kolin Kasashen Afirka a Masar, kakakin shugaban Zimbabwe, George Charamba, yayi watsi da kiraye-kirayen kafa gwamnatin hadin guiwa irin wadda aka yi a kasar Kenya, yana mai fadin cewa ai Zimbabwe ba Kenya ba ce.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Labarai Masu Alaka
Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka Zata Fara Taron Koli Yau Litinin
 
  Muhimmin Labari
Kamfanin Safarar Jirage Ruwa Mafi Girma A Duniya Yace Zai Kaucewa Mashigin Ruwan Aden.

  Karin Labarai
'Yan Bindiga A Yanmkin Niger Delta Sun Kaiwa Kamfanin Shell Hari.
Kungiyar al-Qaida Ta Yi Sako Ga Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama.
'Yan Bindiga Sun Kai Hari A Wani Gari A Somalia Dake Dab Da Kan Iyakarta Da Kenya.
Obama Da McCain Sunyi Alkwari Zasu Yi Aiki Tare.
Rilwan Lukman Yana Cikin Jerin Sunayen Mutane Goma Sha Uku Da Shugaban Najeriya Ya Gabatarwa Majalisar Dattjiai Domin A Nadasu Ministoci.
Hukumar Kiyaye Hakkin Bi'adama Ta Majalisar Dinkin Duniya Tana Kira Ga Isra'ila Ta Janye Kawanya Datakeyiwa Zirin Gaza
India Ta Nutsar Da Jirgin 'Yan Fashin Jirage A Somalia
Shugaban Kwango Laurent Kabila Ya Kori Babban Hafsan Mayakan Kasar,Dakarunsa Suna Ci Gaba Da Shan Kashi A Hanun 'Yan Tawaye.
Shugabannin Kamfanonin Kera Motoci A Amurka, Zasu Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Amurka.
Babban Jirgin Ruwa Dake Dakon Mai Da Aka Sace Ya Kusa Isa Gabar Ruwan Somalia
Iraq Ta Yarda Amurka Taci Gaba Da Kasancewa Cikin Kasar Har Zuwa 2011.
'Yan Bindiga Sun Yi Fashin Wani Jirgin Dakon Kaya A Yankin Niger Deltan Najeriya
'Yan Tawaye A Kwango Sun Sake Kwace Wasu Sabbin Yankuna,A Dai Dai Lokacinda Shugabansu,Lauren Nkunda Ya Gana Da Manzon Majalisar Dinkin Duniya,Janar Obasanjo.
A Yau Litinin,Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama,Yana Ganawa Da Abokin Hamayyarsa A Zaben Shugaban Kasa, John McCain.
Turai Tace Kasashenda Ke Cikin Kungiyar MAsu Aiki Da Kudin Euro Suna Fuskantar Koma Bayan Tattalin Arziki
Pakistan Tana Zargin AMurka Ta Kai Hari Da Makamai Masu Linzami A Yankin Kasar.
Jam'iyyar 'Yan Hamayya MDC A Zimbabwe Tana Taron Koli Domin Tsaida Shawarar Ko Ta Shiga Gwamnatin Hada Kan Kasa
Senata Hillary Clinton Ce Obama Zai Zaba Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka?
An Takaita Ikon Bin Laden A Alkaida
Shugaban Amurka mai Jiran Gado Barack Obama,zai Maye Gurbin Wasu Manyan Jami'an Ayyukan Lelen Asiri Biyu Cikin Watan Janairu
Majalisar Dinkin Duniya Tana Nazarin Bukatar Tura Karin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Kwango
'Yan Bindiga Sun Harbe Wani Ba Amerike  Da Matukinsa Har Lahira A Peshwar.
Sudan Ta Bada Sanarwar Tsagaita Wuta A Yankin Darfur
Shugabannin Amurka Mai Barin Gado George Bush,da Magajinsa Barack Obama, Sun Gana A Fadar White House Jiya Litinin
Hannayen Jari A Kasuwannin Turai da Asiya Sun Yi Kasa A Hada-Hadar Yinin Talata
Wata Kungiyarda Gwamnatin Sudan Ta Kafa Tana Kira Da Tsagaiata Wuta A Fafatawarda Akeyi A Yankin Darfur
Yau Ce Cikar Shekaru 90 Da Kammala Yakin Duniya Na Daya
Miriam Makeba Ta Rasu
Bam Ya Kashe Akalla Mutane Ashirin Da Takwas A Bagadaza
Shugaban Amurka Mai Barin Gado GeorgeBush ,Zai Karbi Bakuncin Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama A Fadar White House.
Shugabannin Siyasar Ivory Coast Sun Fara Taro Domin Tattaunawa Kan  makomar Zaben Kasar Da Ake Yawan Jinkirtawa
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama,Ya Yi Taronsa Farko Da Manema Labaru Tun Bayan Samun Nasara Zabensa
Ban Ki-moon Zai Ziyarci Kwango
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Ya Gana Da Masu Bashi Shawara Kan Harkokin Tattalin Arziki
Obama Ya Fara Tunkarar Tattalin Arziki
Asusun Bada Lamuni(IMF),Yace Tattalin Arzikin Kasashe Da Dama Suna Fuskantar Barazana
Ana Sa Ran Sabon Zababben Shugaban Kasar Amurka Barack Obama Zai Bayyana Sunayen Wasu Manyan Jami'an Gwamnatinsa Bada Jumawa Ba.