Maras Hoto
Search

'Yan Sandan Isra'ila Sun Bada Shawarar A Tuhumi Firayim Minista Ehud Olmert Da Laifuffuka Na Zarmiya

08/09/2008

Ehud Olmert
Ehud Olmert
'Yan sandan bani Isra'ila sun bayyana cewa su na son a tuhumi firayim minista Ehud Olmert a gaban kotu dangane da wani abin fallasa na zarmiya da cin hanci.

Wakilin Muryar Amurka a birnin Qudus, Robert Berger, ya ambaci ・yan sandan su na fadin cewa akwai wadatacciyar shaidar tuhumar firayim minista Olmert da laifuffuka biyu na zarmiya. Suka ce Mr. Olmert ya karya doka ta hanyar karbar takardun ambulon da aka cika da tsabar kudi daga wani bayahude dan kasuwa dan Amurka, da kuma neman da a biya shi sau biyu ko sau uku daga baitulmali na tafiye tafiyen da yayi a waje.

An yi zargin cewa wannan ya faru cikin shekaru 15 da Mr. Olmert yayi yana minista kuma magajin garin birnin Qudus.

Mai fashin bakin harkokin shari・a na Isra・ila, Dan Eisenberg, ya ce atoni janar na Isra・ila ne yake da ikon yanke shawara kan tuhuma, kuma yin hakan yana iya daukar tsawon lokaci.
Eisenberg ya ce, "akwai masu hasashen cewa zai yanke shawara a cikin makonni biyu, amma a gaskiya koda yayi hakan ma, shawarar zata zamo ta wucin gadi ne a saboda tilas ya bada Mr. Olmert damar zuwa a saurare shi kan batun, kuma yin hakan zai dauki watanni. A saboda haka har yanzu za a dauki lokaci mai tsawo kafin a samu shawara ta karshe."

Mr. Olmert ya musanta cewa ya aikata wani laifi, amma a saboda matsin lambar jama・a da kuma jam・iyyarsa, ya shirya yin murabus nan gaba cikin wannan watan. Amma a karkashin tsari mai sarkakiya na gudanar da gwamnati a Isra・ila, yana iya ci gaba da zama kan wannan kujera na karin wata da watanni a matsayin firayim ministan riko.

Mr. Olmert ya ce zai ci gaba da kokarin ganin an samu ci gaba a tattaunawar neman zaman lafiya da Falasdinawa da kuma kasar Syria har ya zuwa ranarsa ta karshe kan wannan kujera.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Kamfanin Safarar Jirage Ruwa Mafi Girma A Duniya Yace Zai Kaucewa Mashigin Ruwan Aden.

  Karin Labarai
'Yan Bindiga A Yanmkin Niger Delta Sun Kaiwa Kamfanin Shell Hari.
Kungiyar al-Qaida Ta Yi Sako Ga Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama.
'Yan Bindiga Sun Kai Hari A Wani Gari A Somalia Dake Dab Da Kan Iyakarta Da Kenya.
Obama Da McCain Sunyi Alkwari Zasu Yi Aiki Tare.
Rilwan Lukman Yana Cikin Jerin Sunayen Mutane Goma Sha Uku Da Shugaban Najeriya Ya Gabatarwa Majalisar Dattjiai Domin A Nadasu Ministoci.
Hukumar Kiyaye Hakkin Bi'adama Ta Majalisar Dinkin Duniya Tana Kira Ga Isra'ila Ta Janye Kawanya Datakeyiwa Zirin Gaza
India Ta Nutsar Da Jirgin 'Yan Fashin Jirage A Somalia
Shugaban Kwango Laurent Kabila Ya Kori Babban Hafsan Mayakan Kasar,Dakarunsa Suna Ci Gaba Da Shan Kashi A Hanun 'Yan Tawaye.
Shugabannin Kamfanonin Kera Motoci A Amurka, Zasu Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Amurka.
Babban Jirgin Ruwa Dake Dakon Mai Da Aka Sace Ya Kusa Isa Gabar Ruwan Somalia
Iraq Ta Yarda Amurka Taci Gaba Da Kasancewa Cikin Kasar Har Zuwa 2011.
'Yan Bindiga Sun Yi Fashin Wani Jirgin Dakon Kaya A Yankin Niger Deltan Najeriya
'Yan Tawaye A Kwango Sun Sake Kwace Wasu Sabbin Yankuna,A Dai Dai Lokacinda Shugabansu,Lauren Nkunda Ya Gana Da Manzon Majalisar Dinkin Duniya,Janar Obasanjo.
A Yau Litinin,Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama,Yana Ganawa Da Abokin Hamayyarsa A Zaben Shugaban Kasa, John McCain.
Turai Tace Kasashenda Ke Cikin Kungiyar MAsu Aiki Da Kudin Euro Suna Fuskantar Koma Bayan Tattalin Arziki
Pakistan Tana Zargin AMurka Ta Kai Hari Da Makamai Masu Linzami A Yankin Kasar.
Jam'iyyar 'Yan Hamayya MDC A Zimbabwe Tana Taron Koli Domin Tsaida Shawarar Ko Ta Shiga Gwamnatin Hada Kan Kasa
Senata Hillary Clinton Ce Obama Zai Zaba Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka?
An Takaita Ikon Bin Laden A Alkaida
Shugaban Amurka mai Jiran Gado Barack Obama,zai Maye Gurbin Wasu Manyan Jami'an Ayyukan Lelen Asiri Biyu Cikin Watan Janairu
Majalisar Dinkin Duniya Tana Nazarin Bukatar Tura Karin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Kwango
'Yan Bindiga Sun Harbe Wani Ba Amerike  Da Matukinsa Har Lahira A Peshwar.
Sudan Ta Bada Sanarwar Tsagaita Wuta A Yankin Darfur
Shugabannin Amurka Mai Barin Gado George Bush,da Magajinsa Barack Obama, Sun Gana A Fadar White House Jiya Litinin
Hannayen Jari A Kasuwannin Turai da Asiya Sun Yi Kasa A Hada-Hadar Yinin Talata
Wata Kungiyarda Gwamnatin Sudan Ta Kafa Tana Kira Da Tsagaiata Wuta A Fafatawarda Akeyi A Yankin Darfur
Yau Ce Cikar Shekaru 90 Da Kammala Yakin Duniya Na Daya
Miriam Makeba Ta Rasu
Bam Ya Kashe Akalla Mutane Ashirin Da Takwas A Bagadaza
Shugaban Amurka Mai Barin Gado GeorgeBush ,Zai Karbi Bakuncin Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama A Fadar White House.
Shugabannin Siyasar Ivory Coast Sun Fara Taro Domin Tattaunawa Kan  makomar Zaben Kasar Da Ake Yawan Jinkirtawa
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama,Ya Yi Taronsa Farko Da Manema Labaru Tun Bayan Samun Nasara Zabensa
Ban Ki-moon Zai Ziyarci Kwango
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Ya Gana Da Masu Bashi Shawara Kan Harkokin Tattalin Arziki
Obama Ya Fara Tunkarar Tattalin Arziki
Asusun Bada Lamuni(IMF),Yace Tattalin Arzikin Kasashe Da Dama Suna Fuskantar Barazana
Ana Sa Ran Sabon Zababben Shugaban Kasar Amurka Barack Obama Zai Bayyana Sunayen Wasu Manyan Jami'an Gwamnatinsa Bada Jumawa Ba.