Dan Majalisar Dattijan Amurka, Democrat Joe Biden,da
Gwmamnan Alaska,Republican Sarah Palin, zasu kara Alhamis din nan,a
muhawara daya rak tsakanin masu takarar mataimakan shugaban kasa.
Ana
sa ran matsalar Tattalin Arziki zata zame babban batu a muhawarar da za a yi a St.
Louis,Missouri,kuma za a maida hankali ainun kan Palin wacce kusan bakuwa ce
sisayar kasa.
Daukar
Sarah Palin a matsayin mataimakiyar shugaban kasa da dan takarar shugabancin
Amurka John Mccain na Republican yayi ya tsuma magoya bayan Jam¡Šiyyar masu
ra¡Šayin rikau,amma masu suka suna shakkar ko tana da kawarewar zama
mataimakiyar shugaban kasa. Mccain a hira da yayi da tashar talabijin na CNN a
yau,ya kare Sarah palin,kuma yace yana da kwarin gwiwa kan kwarewa da
shugabancin ta.
Palin
zata kara da tsohon hanu a Washington, Senator Joe Biden,daga Deleware,wadda
matsalar sa itace tabka kura kurai.