Maras Hoto
Search

Ban Ki-moon Zai Ziyarci Kwango

07/11/2008

People carry their belongings down a road in Mugunga, DRC, 13 Nov. 2007

Sakatare Janar na majalisar Dinkin Duniya, Ba Ki-moon zai sauka a birnin Nairobin Kenya a yau Juma¡Ša, domin halartar wani taro da zai tattauna matsalar Jamhuriyar Kwango ta Kinshasa.

Ana sa ran Shugaban Kwango, Joseph Kabila zai halarci taron, tare da takwaransa na Rwanda Paul Kagame, da wasu shugabannin kasashen Afirka biyar.

Jami¡Šar Diplomasiyyar Amurka, Jendayi Frazier wata kwararriya a kan harkokin Afirka, ita ce zata wakilci Amurka a wajen taron.

A jiya Alhamis Ban Ki-moon yayi kiran da a gaggauta tsagaita wuta a fadan da ake fafatawa a gabashin kasar tsakanin dakarun gwamnati da ¡¥yan tawaye, wanda yayi sanadiyyar mutuwar dubban mutane.

Wata kungiyar kare hakkin dan adam, Human Rights Watch ta fada a jiya Alhamis, cewa an kashe mutum 20, a yakin da suke domin kame kauyen Kiwanja. Kungiyar tace dakarun kiyaye zaman lafiya na Majalisr Dinkin Duniya in banda kallo babu abin da suke tabukawa.

 

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Harin Isra'ila Ya Kasa Raunana Rokokin Hamas

  Karin Labarai
Sojojin Isra'ila Sun Kutsa Cikin Zirin Gaza
Hukumomin Jihar Kano Sun Jefa Alhaji Hamisu Lamido Iyantama A Kurkuku  Audio Clip Available
John Atta-Mills Na Jam'iyyar Hamayya Ta NDC Shi Ne Sabon Shugaban Kasar Ghana
Isra'ila Ta Ce Lokacin Tsagaita Wuta Bai Zo Ba Tukuna
Shugaban Somaliya Yayi Murabus