Shugaban Sudan Omar al-Bashir, ya bada sanarwa
shirin tsagaita wuta kai tsaye ba tareda wani sharadi ba, a arewcin kasar na
yankin Darfur da yaki ya dai-dai ta.
Shugaban yayi kira yau da akawo karshen
fada tsakanin sassa dake gaba da juna,kuma a girke masu sa ido domin tabbatarda cewa duka sassan suna mutunta
yarjejeniyar. Mr. Al-Bashir,yace Sudan zata bullo da shirin kwance damarar
mayakan sakai,kuma ta takaita sojojinta
daga amfani da makamai.
Jiya Talata wata kungiya da ake kira ta wanzarda
Zaman lafiya da enci, ta bada shawarwarin samun zaman lafiya a yankin Darfur,da
ya hada da shirin tsagaita wuta. Kungiyar ta kunshi ministoci da shugabanni
daga Jam'iyun hamayya,kodashike 'yan tawayen yankin Darfur sun kaurace. Cikin
shawarwari da kungiyar ta gabatar harda sakin fursinonin siyasa daga yankin
Darfur,da kuma kirkiro mukamin mataimakin shugaban kasa domin yankin.