Maras Hoto
Search

'Yan Sanda A Indiya Sun Warware Bama-Bamai Guda Biyu...

28/07/2008

dan sanda a Gujarat yana wuce inda bam ya tashiHukumomin Indiya sun warware wasu bama-bamai guda biyu a birnin Ahmedabad, kwana guda a bayan da aka kashe mutane akalla 45 a hare-haren bam a wannan birni.

An gano wadannan bama-bamai jiya lahadi, a lokacin da jami'an tsaro suka bazu a babban birnin harkokin kasuwanci na Jihar Gujarat a yammacin kasar Indiya. A ranar asabar, an kai jerin hare-haren bam biyu a Ahmedabad, inda aka auna wata kasuwar dake cike da mutane da kuma wani asibiti. Mutane 160 suka ji rauni.

'Yan sandan Indiya sun ce an tsare mutane kimanin 30 domin yi musu tambayoyi.

Haka kuma a jiya lahadin, 'yan sanda a Jihar Gujarat sun gano wata mota dauke da nakiyoyi a birnin Surat dake kudu da birnin Ahmedabad. Haka kuma, 'yan sandan Indiya sun kai sumame a kan wani gida a birnin Mumbai. Ana zaton daga wannan gida ne wata wasikar Email dake daukar alhakin kai hare-haren ta fito.

Wata kungiyar da ba a san da ita sosai ba da ta kira kanta Mujahidin ta Indiya, ta dauki alhakin hare-haren a cikin wata wasikar Email da aka aika 'yan mintoci kadan kafin bama-baman su fara tashi.

Ana sa ran firayim ministan Indiya, Manmohan Singh, zai yi tattaki zuwa Ahmedabad yau litinin domin ziyartar wadanda suka ji rauni.
 

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Kamfanin Safarar Jirage Ruwa Mafi Girma A Duniya Yace Zai Kaucewa Mashigin Ruwan Aden.

  Karin Labarai
'Yan Bindiga A Yanmkin Niger Delta Sun Kaiwa Kamfanin Shell Hari.
Kungiyar al-Qaida Ta Yi Sako Ga Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama.
'Yan Bindiga Sun Kai Hari A Wani Gari A Somalia Dake Dab Da Kan Iyakarta Da Kenya.
Obama Da McCain Sunyi Alkwari Zasu Yi Aiki Tare.
Rilwan Lukman Yana Cikin Jerin Sunayen Mutane Goma Sha Uku Da Shugaban Najeriya Ya Gabatarwa Majalisar Dattjiai Domin A Nadasu Ministoci.
Hukumar Kiyaye Hakkin Bi'adama Ta Majalisar Dinkin Duniya Tana Kira Ga Isra'ila Ta Janye Kawanya Datakeyiwa Zirin Gaza
India Ta Nutsar Da Jirgin 'Yan Fashin Jirage A Somalia
Shugaban Kwango Laurent Kabila Ya Kori Babban Hafsan Mayakan Kasar,Dakarunsa Suna Ci Gaba Da Shan Kashi A Hanun 'Yan Tawaye.
Shugabannin Kamfanonin Kera Motoci A Amurka, Zasu Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Amurka.
Babban Jirgin Ruwa Dake Dakon Mai Da Aka Sace Ya Kusa Isa Gabar Ruwan Somalia
Iraq Ta Yarda Amurka Taci Gaba Da Kasancewa Cikin Kasar Har Zuwa 2011.
'Yan Bindiga Sun Yi Fashin Wani Jirgin Dakon Kaya A Yankin Niger Deltan Najeriya
'Yan Tawaye A Kwango Sun Sake Kwace Wasu Sabbin Yankuna,A Dai Dai Lokacinda Shugabansu,Lauren Nkunda Ya Gana Da Manzon Majalisar Dinkin Duniya,Janar Obasanjo.
A Yau Litinin,Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama,Yana Ganawa Da Abokin Hamayyarsa A Zaben Shugaban Kasa, John McCain.
Turai Tace Kasashenda Ke Cikin Kungiyar MAsu Aiki Da Kudin Euro Suna Fuskantar Koma Bayan Tattalin Arziki
Pakistan Tana Zargin AMurka Ta Kai Hari Da Makamai Masu Linzami A Yankin Kasar.
Jam'iyyar 'Yan Hamayya MDC A Zimbabwe Tana Taron Koli Domin Tsaida Shawarar Ko Ta Shiga Gwamnatin Hada Kan Kasa
Senata Hillary Clinton Ce Obama Zai Zaba Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka?
An Takaita Ikon Bin Laden A Alkaida
Shugaban Amurka mai Jiran Gado Barack Obama,zai Maye Gurbin Wasu Manyan Jami'an Ayyukan Lelen Asiri Biyu Cikin Watan Janairu
Majalisar Dinkin Duniya Tana Nazarin Bukatar Tura Karin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Kwango
'Yan Bindiga Sun Harbe Wani Ba Amerike  Da Matukinsa Har Lahira A Peshwar.
Sudan Ta Bada Sanarwar Tsagaita Wuta A Yankin Darfur
Shugabannin Amurka Mai Barin Gado George Bush,da Magajinsa Barack Obama, Sun Gana A Fadar White House Jiya Litinin
Hannayen Jari A Kasuwannin Turai da Asiya Sun Yi Kasa A Hada-Hadar Yinin Talata
Wata Kungiyarda Gwamnatin Sudan Ta Kafa Tana Kira Da Tsagaiata Wuta A Fafatawarda Akeyi A Yankin Darfur
Yau Ce Cikar Shekaru 90 Da Kammala Yakin Duniya Na Daya
Miriam Makeba Ta Rasu
Bam Ya Kashe Akalla Mutane Ashirin Da Takwas A Bagadaza
Shugaban Amurka Mai Barin Gado GeorgeBush ,Zai Karbi Bakuncin Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama A Fadar White House.
Shugabannin Siyasar Ivory Coast Sun Fara Taro Domin Tattaunawa Kan  makomar Zaben Kasar Da Ake Yawan Jinkirtawa
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama,Ya Yi Taronsa Farko Da Manema Labaru Tun Bayan Samun Nasara Zabensa
Ban Ki-moon Zai Ziyarci Kwango
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Ya Gana Da Masu Bashi Shawara Kan Harkokin Tattalin Arziki
Obama Ya Fara Tunkarar Tattalin Arziki
Asusun Bada Lamuni(IMF),Yace Tattalin Arzikin Kasashe Da Dama Suna Fuskantar Barazana
Ana Sa Ran Sabon Zababben Shugaban Kasar Amurka Barack Obama Zai Bayyana Sunayen Wasu Manyan Jami'an Gwamnatinsa Bada Jumawa Ba.