Maras Hoto
Search

Majalisar Dinkin Duniya Tana Nazarin Bukatar Tura Karin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Kwango

12/11/2008

 

A United Nations convoy, heading to Rutshuru in the DRC, crosses a provisional camp for internally displaced persons north of the provincial capital of Goma, 03 Nov  08Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya yana nazarin kira da babban sakataren Majalisar Banki Moon yayi, na neman ya tura karin sojojin kiyaye zaman alfiya a Kwango. 

Babban Sakataren Majalisar Mr. Banki Moon yayi kira da tura karin sojoji dubu uku domin agawaza wadanda ke can da aiki yayiwa yawa a gabashin Kwango,yana cewa lamarin yana kara tabarbarewa. 

Yace fada tsakanin sojojin Gwamnati da 'yan tawaye ya hana kai agaji ga mutane fiyeda dubu dari da yakin ya raba da muhallansu. Ana sa ran kwamitin zai dauki mataki kan bukatar da Mr. Ban ya gabatar masa nan da karshen watan nan. 

Jami'an Majalisar dinkin Duniya sunce ahalin yanzu akwai sojojin Majalisar Dinkin Duniya dubu 17 a Kwango,akasarinsu suna gabshin kasar inda ake fama da tashe tashen hankula. 

Majalisar Dinkin Duniya tana zargin sojojin Gwamnati da yin fyade ga farar hula da dibar ganima a kauyuka dake yankin. Wani kakakin Majalisar Dinkin Duniya yace galibin hare haren suna aukuwa ne a yankunan Kanyabayonga,dake arewacin babban birnin lardi Goma.

 

 

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Harin Isra'ila Ya Kasa Raunana Rokokin Hamas

  Karin Labarai
Sojojin Isra'ila Sun Kutsa Cikin Zirin Gaza
Hukumomin Jihar Kano Sun Jefa Alhaji Hamisu Lamido Iyantama A Kurkuku  Audio Clip Available
John Atta-Mills Na Jam'iyyar Hamayya Ta NDC Shi Ne Sabon Shugaban Kasar Ghana
Isra'ila Ta Ce Lokacin Tsagaita Wuta Bai Zo Ba Tukuna
Shugaban Somaliya Yayi Murabus