Shugaba
Joseph Kabila, na Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango,ya maye gurbin shugaban
rundunar mayakan kasar,yayin da dakarunsa suke ci gaba da fama kan 'yan
tawaye dake ci gaba da dannowa a wani lardin kasar dake gabashi.
A yammacin jiya Litinin ce,shugaba Kabila ya
kori Lt.Janar Dieudonne Kayemba,ya maye gurbinsa da Lt.Janar Didier Etuma. Gidan radiyo da Majalisar Dinkin Duniya yake
gudanarwa da ake kira Okapi,yace sabon hafsan mai shekaru 53 da haifuwa,ya sami
horon soji a Brussels,kuma ya taba rike mukamin babban hafsa mai kula da harkar
mulki na sojojin ruwan Kwango. Dakarun Gwamnatin kasar suna shan kashi a hannun
'yan tawayen dake karkashin bijirarren janar Laurent Nkunda,tun sa'adda 'yan
tawayen suka kaddamar da farmaki a lardin Kivu ta Arewa cikin watan jiya.
Yau
Talata,sojojin Gwamnati sun kara da mayakan sa kai kusa da garin Kanyabayonga.
Madugun mayakan sa kai Sikuli Lafontaine, ya gayawa manema labaru cewa Dakarun
sun kai hari kan mazauna kauyuka,suka kwashi ganima,bayan arangamar da suka
yi dasu.